fidelitybank

Ƴan bindiga sun yi abin gaba da ƴaƴan Sarkin Kagarko da jikokinsa

Date:

Wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun auka Fadar Sarkin Kagarko a kudancin Kaduna, Alhaji Sa’ad Abubakar, inda suka yi awon gaba da ƴaƴansa tara da jikoki da kuma karin mutum uku a garin.

Jaridar Daily Trust ta rawaito wani mazaunin garin, na cewa ƴan bindigar sun kutsa yankin ne cikin dare kamar ƙarfe 11:15 na dare inda kuma suka nufi fadar Sarkin.

“Sun kuma tafi da amaryar sarkin da yaransa tara da jikokinsa amma matar ta kuɓuta, inda ta dawo gida,” in ji shi.

A cewar mazaunin, ƴan bindigar sun kuma yi garkuwa da karin mutum uku ciki har da wata mata, tare da raunata wani Audu Kwakulu na Unguwar Pah wanda a halin yanzu yake samun kulawa a asibiti.

“Ƴan bindigar sun kuma kashe wani makiyayi a ƙauyen Kuchimi tare da sace kaya a shaguna bakwai a kauyen Janjala duka a karamar hukumar Kagarko – a hanyarsu ta komawa,” kamar yadda majiyar ta bayyana.

Kakakin rundunar ƴan sandan Kaduna, DSP Muhammed Jalige bai amsa kiran da BBC ta yi masa game da wannan labari ba.

Kaduna dai ɗaya ce daga cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya da ke fama da matsalar tsaro a ƙasar.

Ƴan bindiga sun sha kai hare-hare a sassa daban daban na jihar, yayin da gwamnati ta sha yin alƙawarin magance matsalar.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp