Wasu ‘yan bindiga sun sake kai hari garin Kagoro da ke garin Mallagum-Kagoro a karamar hukumar Kaura a jihar Kaduna.
Jaridar DAILY POST ta rawaito cewa an sake kai wa al’ummar Kudancin Kaduna hari a daren Juma’a, kwana guda bayan da aka yi jana’izar wadanda aka kashe a baya.
An kai harin ne tsakanin sa’o’i 9 na dare zuwa karfe 10 na dare inda ‘yan bindigar suka fara harbe-harbe kai-tsaye.
Wata majiya da ta zanta da DAILY POST, ta bayyana cewa ‘yan bindigar sun zo da adadi mai yawa, dauke da muggan makamai.
Ya kara da cewa, “Yayin da ‘yan bindigar ke ta harbe-harbe a kaikaice, kuma jama’a na gudun hijira, matakin da sojoji suka yi a kan lokaci ya ceci lamarin, kuma ba a samu asarar rai ba.”
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Muhammed Jalige bai samu jin ta bakinsa ba.