fidelitybank

Ƴan bindiga sun sake dace wasu Mata biyu a Abuja

Date:

Wasu ‘yan bindiga su shida sun far wa wani gida a kauyen Guita da ke Chikakore, a yankin Kubwa da ke Abuja inda suka yi awon gaba da ‘yan mata guda biyu ‘yan uwan juna masu shekaru 16 da 14.

Bayan kwashe ‘yan matan ne kuma ‘yan bindigar suka ranta a na kare inda suka shiga daji wanda ya hada kauyen da wasu kauyukan masu makwabtaka.

Wani shaida ya fada wa jaridar Daily Trust cewa ” la ranar Lahadi lokacin da ‘yan bindigar suka je sun kutsa gidan ne ba tare da harbi irin na kan-mai-uwa-da-wabi ba kamar yadda suka saba sannan suka kama ‘yan matan guda biyu.”

Wannan ne dai karo na biyu a kasa da wata guda da ‘yan bindiga ke yin garkuwa da ‘yan mata ‘yan uwan juna a babban birnin na tarayya.

Batun tsaro na kara ta’azzara a birnin na Abuja wani abu da ke kara jefa fargaba a zukatan mazauna birnin.

To sai dai a baya rundunar ‘yan sandan birnin ta sha cewa tana iya bakin kokarinta wajen ganin su dakile matsalar.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya na murkushe ‘Yan adawa – Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ce...

Gwamnatin Kano ta baiwa yara fifiko – UNICEF

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya...

Majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 21

A ranar Talata ne majalisar Dattawa ta amince da...

An sallami Gwamnan Katsina daga asibiti bayan ya samu rauni a hatsarin mota

An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,...

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...
X whatsapp