An yi garkuwa da al’ummar kauyen Matusji fiye da 10 a karamar hukumar Talata Mafara a jihar Zamfara.
Daga cikin wadanda abin ya shafa har da majiyyaci.
Wani magidanci mai suna Ahmad Babangida ya shaidawa manema labarai cewa, ‘yan bindigar sun afkawa al’umma da manyan makamai inda suka fara harbe-harbe kai tsaye da misalin karfe 2:30 na daren ranar Juma’a.
“Dukkanmu muna barci amma tsananin karar harbin bindigar ya tashe mu kuma kowa ya fara gudu”, in ji shi.
Ya ce ko da yake babu wanda ya rasa ransa a harin, amma ‘yan bindigar sun tafi da mutane da dama zuwa inda ba a san inda suke ba.
“’Yan fashin ba su ce komai ba dangane da batun kudin fansa. Ba mu san inda mutanenmu suke ba,” in ji shi.
A cewarsa, wadanda aka sace sun hada da majinyaci da ke karbar magani yayin da yake kan diga IV, yana mai nuni da cewa mutanen kauyen ba su farfaɗo ba daga fargabar.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazeed Abubakar ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce ‘yan bindigar sun yi garkuwa da mutane 10.
Ya kuma kara da cewa, rundunar ‘yan sandan ta baza jami’an ‘yan sanda masu dabara domin kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su tare da cafke ‘yan fashin.