fidelitybank

Ƴan bindiga sun sace mutane 10 a Zamfara

Date:

An yi garkuwa da al’ummar kauyen Matusji fiye da 10 a karamar hukumar Talata Mafara a jihar Zamfara.

Daga cikin wadanda abin ya shafa har da majiyyaci.

Wani magidanci mai suna Ahmad Babangida ya shaidawa manema labarai cewa, ‘yan bindigar sun afkawa al’umma da manyan makamai inda suka fara harbe-harbe kai tsaye da misalin karfe 2:30 na daren ranar Juma’a.

“Dukkanmu muna barci amma tsananin karar harbin bindigar ya tashe mu kuma kowa ya fara gudu”, in ji shi.

Ya ce ko da yake babu wanda ya rasa ransa a harin, amma ‘yan bindigar sun tafi da mutane da dama zuwa inda ba a san inda suke ba.

“’Yan fashin ba su ce komai ba dangane da batun kudin fansa. Ba mu san inda mutanenmu suke ba,” in ji shi.

A cewarsa, wadanda aka sace sun hada da majinyaci da ke karbar magani yayin da yake kan diga IV, yana mai nuni da cewa mutanen kauyen ba su farfaɗo ba daga fargabar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazeed Abubakar ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce ‘yan bindigar sun yi garkuwa da mutane 10.

Ya kuma kara da cewa, rundunar ‘yan sandan ta baza jami’an ‘yan sanda masu dabara domin kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su tare da cafke ‘yan fashin.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp