fidelitybank

Ƴan Bindiga sun sace matafiya da dama a Zamfara

Date:

Wasu da ake zargin ƴan bindiga sun toshe babbar hanyar Gusau zuwa Funtua mai cike da cunkoso tare da yin awon gaba da matafiya da dama.

Ƴan bindigar sun tare babbar hanyar da ke tsakanin al’ummar Kucheri da Magazu a karamar hukumar Tsafe, inda suka yi ta harbin kan mai uwa da wabi.

Mai magana da yawun ƴansandan jihar ta Zamfara, ASP Yazid Abubakar, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ga gidan talabijin na Channels, ya ce an yi garkuwa da mutanen da ba a tantance adadinsu ba a harin.

Ya ce jami’an tsaro na can suna hoɓɓasa don ganin an ceto mutanen da aka tafi da su.

“Lamarin ya faru ne da yammacin jiya Asabar. Ƴan bindigar sun tare hanya suka fara harbin kan masu tafiya inda suka yi garkuwa da wasu daga cikinsu,” inji kakakin ƴansandan.

Ya ce jami’ansu tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro suna aiki tare don ganin an ceto waɗanda aka sace.

Sai dai Abubakar ya musanta rahotannin da ke cewa an yi garkuwa da ‘yansanda biyar a lokacin da suke artabu da ‘yan bindigar.

Zamfara dai na ɗaya daga cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya da ke fama da hare-haren gungun ‘yan bindiga, waɗanda ke yin garkuwa da jama’a domin neman kuɗin fansa.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp