fidelitybank

Ƴan bindiga sun kashe mutum 12 da ƙona gidaje a Neja

Date:

Rahotanni daga ƙaramar hukumar mulkin Shiroro a jihar Neja na cewa, wasu da ake zargin mayaƙan kungiyar Boko Haram ne sun kashe sama da mutum goma sha biyu tare da ƙona kimanin gidaje talatin a wasu jerin hare-hare da suka kai.

Mazauna yankunan sun ce hare-haren sun faru ne a tsawon makon da ya gabata, a garuruwan Alawa da Bangajiya da sauran su, inda baya ga kashe mutane da dama da maharan suka yi sun kuma yi awon gaba da dukiya mai ɗimbin yawa.

Wani Mazaunin garin ya shaida wa BBC cewar sama da makonni biyu ke nan suke fama da tashe tashen hankula na hare-haren ƴan bindiga waɗanda suka hana su sukuni.

A cewar sa, a makon da ya gabata ne ƴan bindigar suka dasa bam a hanya wanda ya tashi da wasu da ke kan hanyar komawa ƙauyukansu daga kasuwa kuma nan take mutane aƙalla takwas suka rasa rayukansu.

Da aka je kwashe gawawwakin waɗanda aka kashe kuma aka sake kai wani harin da ya yi sanadiyar asarar rayuka sannan suka hana daukar gawawwakin wanda har ya zuwa yanzu babu labarin kwashe gawawwakin.

Shugaban ƙaramar Hukumar Shiroro Hon. Akiku Kuta ya tabbatar da harin

Wadannan sabbin hare-haren dai sun sa mutane da dama yin hijira zuwa wasu makwabtan garuruwa

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp