Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kashe mutane da dama tare da yin garkuwa da wasu a kauyen Gada da ke karamar hukumar Bungudu a jihar Zamfara.
Wani dan kauyen mai suna Ibrahim Musa ya bayyana haka a wata hira da manema labarai ta wayar tarho cewa yan ta’addan sun kai farmaki kauyen ne da misalin karfe 6 na yammacin ranar Asabar.
“’Yan bindigar dauke da manyan muggan makamai, sun iso kan babura da yawa kuma suka fara harbi ba kakkautawa kan mutanen kauyen. Mun yi asarar mutane bakwai a wannan danyen aikin, inda aka yi garkuwa da mutane da dama,” ya kara da cewa.
Rahotanni na cewa harin ya faru ne kwana guda bayan da gwamnan ya tafi jihar Imo domin jagorantar tawagar jam’iyyar PDP a zaben gwamna.
Musa ya bukaci gwamnatin tarayya da ta sa baki wajen ceto al’ummar jihar Zamfara, ganin yadda lamarin ke kara ta’azzara.
“Babu wanda yake cikin koshin lafiya a jihar, kuma muna rokon gwamnatin tarayya da ta kara tura jami’an tsaro a jihar Zamfara domin dakile ayyukan ‘yan bindigar da suka addabi jihar.”
Kokarin da manema labarai suka yi a Gusau babban birnin jihar domin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazid Abubakar, ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.