fidelitybank

Ƴan bindiga sun kashe mutane 7 a Zamfara

Date:

Kimanin sa’o’i 24 da ‘yan bindiga suka kashe mutane 56 a kauyuka uku da ke karamar hukumar Bakura ta jihar Zamfara, wasu ‘yan bindiga sun sake kashe wasu mutane bakwai a karamar hukumar Maradun ta jihar.

Kananan hukumomin Maradun da Bakura sun raba kan iyaka.

A sabon harin da aka kai da yammacin ranar Asabar, wata majiya a Maradun ta ce, an kai hari kauyuka biyu Faru da Kauyen Minane.

“Ina babban asibitin Maradun lokacin da sojoji suka kawo gawarwakin wadanda aka kashe,” in ji Jamilu Muhammad.

“Mutanen mu da ke kauyen Garin Minane sun ce ‘yan bindigar sun kai farmaki garin ne da misalin karfe 2 na rana inda suka fara harbe-harbe kai tsaye. Abin da suka saba yi shi ne gida-gida don neman dabbobin gida ko wasu kayayyaki masu daraja amma a jiya da suka shiga kauyen sai suka fara harbe-harbe ba da dadewa ba,” inji shi.

A cewarsa, an kashe mutane shida a Garin Minane yayin da aka kashe daya a Faru. Ya ce adadin wadanda aka kashe na iya karuwa saboda da yawa sun bace a kauyukan da lamarin ya shafa.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...
X whatsapp