fidelitybank

Ƴan bindiga sun kashe mutane 18 a Binuwai

Date:

Mutum aƙalla 18 ne suka rasa rayukansu bayan wani hari da ‘yan bindiga suka kai a yankin Ukohol na Ƙaramar Hukumar Guma da ke Jihar Binuwai.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito mai bai wa shugaban karamar hukumar shawara kan harkar tsaro Christopher Waku na cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 5:00 na yammacin Alhamis lokacin da mutane suke tsaka da cin kasuwa a yankin.

Ya kuma ce ana ci gaba da bincike domin gano wadanda suka ɓata.

Shi ma shugaban karamar hukumar, Mike Ubah, ya tabattar wa manema labarai faruwar lamarin, inda ya ce ‘yan bindigar sun je wurin ne sanye da baƙaken kaya, kuma da isarsu suka buɗe wa mutane wuta a cikin kasuwar, inda nan take 10 suka mutu.

Ubah ya kara da cewa bayan haka sun kai hare-hare a kauyuka da ke kusa tare da kashe mutum takwas.

Mai magana da yawun ‘yan sandan Binuwai, SP Catherine Anene, ta tabbatar da kai harin amma ta ce ba su da wasu bayanai ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp