Mutum aƙalla 18 ne suka rasa rayukansu bayan wani hari da ‘yan bindiga suka kai a yankin Ukohol na Ƙaramar Hukumar Guma da ke Jihar Binuwai.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito mai bai wa shugaban karamar hukumar shawara kan harkar tsaro Christopher Waku na cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 5:00 na yammacin Alhamis lokacin da mutane suke tsaka da cin kasuwa a yankin.
Ya kuma ce ana ci gaba da bincike domin gano wadanda suka ɓata.
Shi ma shugaban karamar hukumar, Mike Ubah, ya tabattar wa manema labarai faruwar lamarin, inda ya ce ‘yan bindigar sun je wurin ne sanye da baƙaken kaya, kuma da isarsu suka buɗe wa mutane wuta a cikin kasuwar, inda nan take 10 suka mutu.
Ubah ya kara da cewa bayan haka sun kai hare-hare a kauyuka da ke kusa tare da kashe mutum takwas.
Mai magana da yawun ‘yan sandan Binuwai, SP Catherine Anene, ta tabbatar da kai harin amma ta ce ba su da wasu bayanai ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoton