fidelitybank

Ƴan bindiga sun kashe jami’an tsaro bakwai a Imo

Date:

Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kashe wasu jami’an tsaron gida bakwai da ke bakin aiki a Umuafom, Orogwe a karamar hukumar Owerri ta yamma a jihar Imo.

‘Yan bindigar da suka mamaye yankin a ranar Litinin din da ta gabata, sun kuma raunata wasu mazauna yankin da aka ce halin da suke ciki na cikin mawuyacin hali a asibiti.

Wata majiya daga al’ummar yankin ta shaida wa jaridar The Nation cewa, ‘yan bindigar wadanda suka zo a cikin motoci biyu da misalin karfe 9 30 na dare, sun dauki masu gadin ne ba tare da saninsu ba, suka harbe su a wurare daban-daban.

Wasu biyu kuma sun fada hannun ‘yan bindigar yayin da suke kokarin tserewa domin tsira. An harbe daya daga cikin wanda abin ya shafa, dan babur din kasuwanci ne a kafarsa kuma babur din ya kwace shi. An ce yana karbar magani a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya, (FMC) Owerri, yayin da aka yi wa dayan da aka yi masa yankan adda.

KARANTA WANNAN: ‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane biyu a Oyo

An shiga fargaba a cikin al’ummar yankin biyo bayan harin yayin da wasu daga cikin mazauna yankin ke barin matsugunin su na wani dan lokaci domin tsira da rayukansu.

Kakakin ‘yan sandan Imp, Michael Abattam ya tabbatar da faruwar lamarin.

Sai dai ya ce, har yanzu bai iya tantance ko wadanda aka kashen jami’an tsaro ne ba.

Ya kuma tabbatar da cewa, tuni ‘yan sanda suna bin wadanda ake zargin, inda ya roki jama’a da su kwantar da hankalinsu, kada su firgita.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp