fidelitybank

Ƴan bindiga sun kashe Ɗan Sanda bayan sun yi masa kwanta Ɓauna

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Ebonyi, a ranar Talata, ta tabbatar da kisan wani jami’in ta da wasu ‘yan bindiga suka yi masa kwanta ɓauna a zagayen bankin Union, Abakaliki, babban birnin jihar.

Wanda aka kashe, wanda har yanzu ba a bayyana sunansa ba, har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, ‘yan bindigar sun kashe shi ne a daren ranar Litinin, yayin da wasu ‘yan sanda biyu suka samu munanan raunukan harbin bindiga.

Rahotanni na cewa, jami’an ‘yan sandan sun tsaya suna aikin bincike a zagayen bankin Union, unguwar da bankunan suka fi yawa a cikin babban birnin jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ebonyi, CP. Faleye Olayele ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Onome Onovwakpoyeya ya rabawa manema labarai.

Kwamishinan ya ce: “Jami’an ‘yan sandan da ke aikin tsayawa da bincike a zagayen bankin Union, yankin da bankunan ke da babban birnin jihar, sun yi artabu da ‘yan bindiga dauke da muggan makamai, wadanda ba a san inda suke ba.

“Abin bakin ciki ne, daya daga cikin jami’an ya biya farashi mai tsoka, yayin da wasu biyu suka samu raunuka kuma suna karbar magani a asibiti. Har ila yau, ’yan bindigar sun yi asarar rayuka, amma an tafi da su. ”

Kwamishinan ya sha alwashin tabbatar da cewa an gurfanar da wadanda suka kashe a gaban kuliya domin amsa laifin da suka aikata a jihar.

“Ya kamata jama’a su kwantar da hankalinsu, saboda an dauki matakan kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa,” in ji shi.

Olayele ya yi kira ga jama’a da su kai rahoton duk wanda aka gani da raunin harsashi ko kuma ya nemi a yi masa magani a jihar.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp