fidelitybank

Ƴan bindiga sun kashe Ɗan Sanda bayan sun yi masa kwanta Ɓauna

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Ebonyi, a ranar Talata, ta tabbatar da kisan wani jami’in ta da wasu ‘yan bindiga suka yi masa kwanta ɓauna a zagayen bankin Union, Abakaliki, babban birnin jihar.

Wanda aka kashe, wanda har yanzu ba a bayyana sunansa ba, har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, ‘yan bindigar sun kashe shi ne a daren ranar Litinin, yayin da wasu ‘yan sanda biyu suka samu munanan raunukan harbin bindiga.

Rahotanni na cewa, jami’an ‘yan sandan sun tsaya suna aikin bincike a zagayen bankin Union, unguwar da bankunan suka fi yawa a cikin babban birnin jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ebonyi, CP. Faleye Olayele ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Onome Onovwakpoyeya ya rabawa manema labarai.

Kwamishinan ya ce: “Jami’an ‘yan sandan da ke aikin tsayawa da bincike a zagayen bankin Union, yankin da bankunan ke da babban birnin jihar, sun yi artabu da ‘yan bindiga dauke da muggan makamai, wadanda ba a san inda suke ba.

“Abin bakin ciki ne, daya daga cikin jami’an ya biya farashi mai tsoka, yayin da wasu biyu suka samu raunuka kuma suna karbar magani a asibiti. Har ila yau, ’yan bindigar sun yi asarar rayuka, amma an tafi da su. ”

Kwamishinan ya sha alwashin tabbatar da cewa an gurfanar da wadanda suka kashe a gaban kuliya domin amsa laifin da suka aikata a jihar.

“Ya kamata jama’a su kwantar da hankalinsu, saboda an dauki matakan kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa,” in ji shi.

Olayele ya yi kira ga jama’a da su kai rahoton duk wanda aka gani da raunin harsashi ko kuma ya nemi a yi masa magani a jihar.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp