Rahotanni daga jihar Kebbi a arewa maso yammacin Najeriya na cewa kimanin mutum 20 ne suka rasa rayukansu a wasu hare-hare da wasu ƴan bindiga suka kai a wasu garuruwa biyu a jiya Lahadi.
Lamarin ya faru ne a yankin karamar Hukumar Augie – ɗaya daga cikin yankunan da ake cewa mayaƙan Lakurawa na da sansani.
Kodayake kawo yanzu ba a tabbatar ko su wa ne maharan ba.
Ga dai karin bayanin da Jameel Gulma wani ɗan jarida a yankin da ya bibiyi labarin, inda ya ce maharan sun kashe mutum shida ne, suka kwashe shanu, sai ƴan sa-kai suka bi su.
“A nan suka yi wa ƴan sa-kan kwantan ɓauna, suka buɗe musu wuta, inda suka kashe guda 13 daga cikinsu.”