fidelitybank

Ƴan bindiga sun harbe mutum guda a Edo

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun kashe wani mutum mai suna Emmanuel Rufus a jihar Edo.

Lamarin ya faru ne a ranar Asabar a hanyar Igarra-Ebilo a karamar hukumar Akoko-Edo a jihar, kamar yadda NAN ta ruwaito.

Wata majiya da ta so a sakaya sunanta ta ce wanda abin ya shafa na tafiya ne tare da ‘yan uwansa biyu a cikin wata mota kirar Mercedes-Benz GLK a lokacin da ‘yan bindigar suka fito daga daji suka bude wa motar wuta.

Daya daga cikin wadanda abin ya rutsa da su ya mutu a cikin wannan tsari, yayin da sauran mutanen da ke cikin motar suka tafi da su cikin daji.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Edo, SP Chidi Nwabuzor, wanda ya tabbatar da kisan, ya ce ba batun yin garkuwa da mutane ba ne, illa dai kisan kai ne.

Nwabuzor ya ce, rahoton da jami’in ‘yan sanda reshen yankin Igarra ya fitar ya nuna cewa an ga wani Emmanuel Rufus a kwance a kan titin Igarra-Ebilo a karamar hukumar Akoko Edo ta jihar.

Ya ce ‘yan sanda da ’yan banga sun yi tattaki zuwa wurin, inda suka gamu da wanda abin ya faru da harbin bindiga a cikin motar, mai lamba BEN 303 GM.

Kakakin ’yan sandan ya ce daga baya danginsa suka dauki gawar marigayin domin binne shi.

A cewarsa, ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin, tare da kokarin cafke wadanda ake zargi da guduwa.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp