fidelitybank

Ƴan bindiga sun harbe mutum guda a Edo

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, sun kashe wani mutum mai suna Emmanuel Rufus a jihar Edo.

Lamarin ya faru ne a ranar Asabar a hanyar Igarra-Ebilo a karamar hukumar Akoko-Edo a jihar, kamar yadda NAN ta ruwaito.

Wata majiya da ta so a sakaya sunanta ta ce wanda abin ya shafa na tafiya ne tare da ‘yan uwansa biyu a cikin wata mota kirar Mercedes-Benz GLK a lokacin da ‘yan bindigar suka fito daga daji suka bude wa motar wuta.

Daya daga cikin wadanda abin ya rutsa da su ya mutu a cikin wannan tsari, yayin da sauran mutanen da ke cikin motar suka tafi da su cikin daji.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Edo, SP Chidi Nwabuzor, wanda ya tabbatar da kisan, ya ce ba batun yin garkuwa da mutane ba ne, illa dai kisan kai ne.

Nwabuzor ya ce, rahoton da jami’in ‘yan sanda reshen yankin Igarra ya fitar ya nuna cewa an ga wani Emmanuel Rufus a kwance a kan titin Igarra-Ebilo a karamar hukumar Akoko Edo ta jihar.

Ya ce ‘yan sanda da ’yan banga sun yi tattaki zuwa wurin, inda suka gamu da wanda abin ya faru da harbin bindiga a cikin motar, mai lamba BEN 303 GM.

Kakakin ’yan sandan ya ce daga baya danginsa suka dauki gawar marigayin domin binne shi.

A cewarsa, ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin, tare da kokarin cafke wadanda ake zargi da guduwa.

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp