Rundunar ƴan sanda a jihar Katsina ta tabbatar da kisan wani kansila a ƙaramar hukumar Funtua da ke jihar Katsina.
Lamarin ya faru ne a daren ranar Litinin sa’ilin da ƴan bindigar suka kai hari a unguwar Nasarawa da ke a karamar hukumar ta Funtua.
A tattaunawar da ya yi da BBC, mai magana da yawun rundunar ƴansandan Najeriya a jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce bayanan da suka tattara sun tabbatar da mutuwar kansilan mai suna Samaila Buhari Mairago.
Iyalan mamacin sun ce tuni aka yi jana’izar sa a yau Talata.
Funtua na ɗaya daga cikin yankunan da ke fama da matsalar tsaro ta ƴan fashin daji a jihar ta Katsina.
Kuma yankin na maƙwaftaka da jihar Zamfara, wadda matsalar tsaron ta yi wa ƙamari.