fidelitybank

Ƴan bindiga sun harbe jami’in INEC a Imo

Date:

 

An harbe Nwokorie Anthony, jami’in Hukumar Zabe mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC a Jihar Imo.

An kashe jami’in ne a yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin rijistar zaɓe (CVR) a Ƙaramar Hukumar Ihitte Uboma da ke jihar.

A cewar Kwamishinan Zabe na jihar, Resident, Farfesa Emeka Ezeonu, an kashe Nwokorie ne a Nkwo Ihitte (mazaɓar 004) da ke mazaɓar Amakohia (RA 02) na Ƙaramar Hukumar Ihitte Uboma, sannan ba a san inda wasu ma’aikatan biyu da ke aikin rajistar su ke ba. .

A bisa wannan mumunan lamarin, hukumar zaɓen ta dakatar da gudanar da aikin rijistar katin zaɓen a karamar hukumar.

Kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kaɗa kuri’a, Festus Okoye ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.

Kafin faruwar wannan lamari, hukumar ta dakatar da CVR a Ƙananan Hukumomin Osu da Njaba na jihar saboda rashin tsaro, yayin da ake gudanar da aikin a ofishin INEC na Ƙaramar Hukumar Oru Gabas, Oru ta Yamma, Orlu da Ohaji-Egbema.”

“Hukumar na mika ta’aziyyarta ga iyalan Nwokorie Anthony tare da addu’ar Allah ya basu ikon jure rashin. An kai rahoton faruwar lamarin ga jami’an tsaro domin bankado al’amuran da suka haifar da wannan mummunan lamari tare da gurfanar da masu laifin a gaban kuliya,” inji Okoye.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp