fidelitybank

Ƴan bindiga sun harbe jami’in INEC a Imo

Date:

 

An harbe Nwokorie Anthony, jami’in Hukumar Zabe mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC a Jihar Imo.

An kashe jami’in ne a yayin da ake ci gaba da gudanar da aikin rijistar zaɓe (CVR) a Ƙaramar Hukumar Ihitte Uboma da ke jihar.

A cewar Kwamishinan Zabe na jihar, Resident, Farfesa Emeka Ezeonu, an kashe Nwokorie ne a Nkwo Ihitte (mazaɓar 004) da ke mazaɓar Amakohia (RA 02) na Ƙaramar Hukumar Ihitte Uboma, sannan ba a san inda wasu ma’aikatan biyu da ke aikin rajistar su ke ba. .

A bisa wannan mumunan lamarin, hukumar zaɓen ta dakatar da gudanar da aikin rijistar katin zaɓen a karamar hukumar.

Kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kaɗa kuri’a, Festus Okoye ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.

Kafin faruwar wannan lamari, hukumar ta dakatar da CVR a Ƙananan Hukumomin Osu da Njaba na jihar saboda rashin tsaro, yayin da ake gudanar da aikin a ofishin INEC na Ƙaramar Hukumar Oru Gabas, Oru ta Yamma, Orlu da Ohaji-Egbema.”

“Hukumar na mika ta’aziyyarta ga iyalan Nwokorie Anthony tare da addu’ar Allah ya basu ikon jure rashin. An kai rahoton faruwar lamarin ga jami’an tsaro domin bankado al’amuran da suka haifar da wannan mummunan lamari tare da gurfanar da masu laifin a gaban kuliya,” inji Okoye.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp