Yan bindiga sun kashe mutum 34 a wani hari da suka kai sansanin ‘yan gudun hijita da ke wata makarantar firaimari a ƙauyen Mgaban da ke Ƙaramar Hukumar Benue ta Arewa a daren Juma’a.
Wani mazaunin yankin ya shaida wa jaridar Daily Trust cewa maharan sun isa ƙauyen ne da misalin ƙarfe 9 na dare Juma’a.
Ya ce cikin waɗanda aka kashe akwai wata mata mai ciki da ɗanta sannan kuma da dama sun jikkata.
Ka zalika mai bayar da shawara kan harkokin tsaro na Ƙaramar Hukumar Guma Christopher Waku, ya shaida wa jaridar cewa an kashe mutum 34 yayin da aka jikkata wasu 40 na daban.
Kakakin ‘yan sanda ta jihar SP Catherine Anene, ta tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar sakon waya da ta turawa wakilin jiridar, sai dai ba ta yi wani cikakken ƙarin bayani ba.