fidelitybank

Ƴan bindiga sun bayar da dala 3,000 ga wasu mutane a Zamfara

Date:

Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindiga sun biya wasu al’ummomi uku a karamar hukumar Shinkafi da ke jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya Naira miliyan 3 kowannensu (kimanin dalar Amurka $3000), domin a biya wani kasurgumin dan fashin da aka fi sani da Dan Bokolo, domin dakile hare-haren da kungiyar ke kaiwa al’umomin.

Akwai rahotannin cewa harajin tarar ne ga al’ummomin da suka bayar da bayanai ga jami’an tsaro da mazauna garuruwan Kamarawa, Sabuwar Kamarawa, da Gebe suka yi, wanda ya kai ga cafke dan uwan Dan Bokolo, Abdullahi.

Yayin da gwamnan jihar, Dauda Lawal, ya tsaya tsayin daka kan tattaunawa da ‘yan ta’adda, majiyoyin yankin sun yi ikirarin cewa an biya kudin ne domin tabbatar da tsaron lafiyar al’umma.

Wani mazaunin garin da ya yi magana da boye sunansa ya ce kama Abdullahi ya jawo tashin hankali a cikin al’ummomin inda Dan Bokolo ya ce wasu daga cikin al’ummomin sun ci amanar dan uwansa.

A kokarin samar da zaman lafiya, dattawan al’umma sun shiga tattaunawa da ‘yan ta’adda. Daga karshe Dan Bokolo ya amince ya karbi rangwamen kudi Naira miliyan 3, daga farkon bukatarsa ta Naira miliyan 6, a matsayin diyya kan cin amanar da aka yi masa.

Wani mai fafutukar neman zaman lafiya kuma mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Basharu Guyawa ya bayyana cewa irin wannan harajin kariya ya zama ruwan dare gama gari a Gabashin Sakkwato da Zamfara.

A yayin da al’ummomin suka bayar da rahoton biyan bukatun, har yanzu akwai damuwa game da kudurin ‘yan bindigar na kauracewa kai hare-hare a nan gaba, in ji NEWSng.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp