Babban Fasto na Cocin Divine Mercy, Olatobiloba Peters ya yi hasashen cewa ƴan jam’iya mai mulki ta APC za su ci kuɗin Bola Ahmed Tinubu ne kawai su kuma ko zabar sa.
Ya kuma gargaɗi Tinubun, mai neman tsayawa takarar shugaban ƙasa a 2023 da kada ya ci gaba da burinsa na zama shugaban ƙasa.
Fasto Peters ya ce ƴan jam’iyyar APC, za su karɓi kuɗin Tinubu kawai kuma su ƙi kaɗa masa ƙuri’a.
Da yake zantawa da DAILY POST, limamin ya ce Ubangiji ne ya nuna masa cewa ‘yan APC za su yi amfani da kudin Tinubu su cicciɓa mataimakin shugaban kasa, Osinbajo ya zama shugaban kasa.
Tinubu, wanda ya sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari aniyarsa ta tsayawa takarar shugabancin kasar a 2023, ya ce matakin wani buri ne a gare shi tsawon rayuwarsa.
Jagoran jam’iyyar APC na Ƙasa ya ce yana ci gaba da tuntuɓar masu ruwa da tsaki a kan matakin da ya ɗauka na maye gurbin Buhari a 2023.
Sai dai Fasto Peters ya ce Ubangiji ya halicci Tinubu ne domin ya kafa sarakuna ba wai shi ya zama ba.
Limamin ya bukaci tsohon gwamnan jihar Legas ɗin da kada ya barnatar da kudinsa a kan kudirinsa na shugaban kasa.
Sai dai ya yi gargadin cewa ‘yan Najeriya za su yi nadama idan har Tinubu ya tilasta wa kan sa mulki ta hanyar magudi.