Shugaban ƙasar Ghana Nana Akufo-Addo, ya sanar da cewa dukan ƴan ƙasashen nahiyar Afika za su iya shiga ƙasarsa ba tare da takardar izinin ba wato biza.
Da wannan sanarwa a yanzu Ghana ta bi sahun wasu ƙasashe irin su Rwanda da Seychelles da Gambia da kuma jumhuriyar Benin da suka sauƙaƙawa ƴan Afrika shiga ƙasarsu ba tare da biza ba.
Shugaban ya ɗauki wannan matakin a daidai lokacin da yake ban-kwana da shugabancin ƙasar, bayan tsohon tsohon Shugaban Ƙasar John Mahama ya kayar da mataimakinsa shugaban na yanzu a zaɓen shugaban ƙasar