Kimanin mutane 100 ‘yan asalin Afirka ne suke kewaye da tawagar ‘yan sanda a gundumar Neb Sarai da ke Kudancin Delhi a ranar Asabar din da ta gabata, inda suka yi arangama da su tare da kuɓutar da wasu ‘yan Najeriya da aka tsare saboda kare lafiyarsu ta hanyar amfani da muggan kwayoyi.
An kai wadanda ake tsare da su ofishin ‘yan sanda.
Tawagar jami’an masu kula da safarar miyagun kwayoyi ta tafi da misalin karfe 2:30 na rana zuwa Raju Park da ke Neb Sarai a Indiya, domin gudanar da aikin korar wasu ‘yan kasashen waje da suka wuce inda suka dauko wasu ‘yan Najeriya uku wadanda takardar izinin shiga kasar ta kare.
A halin da ake ciki kuma, wasu gungun mutane sama da 100 ‘yan asalin Afirka sun kewaye su tare da kawo cikas ga aikin ‘yan sanda.