fidelitybank

Ƴan ƙasa ku nemi taimakon Allah shi yafi sauki – IBB

Date:

Tsohon shugaban mulkin sojan Najeriya, Ibrahim Badamasi Babangida, ya ja hankalin ‘yan kasa a kan su nemi taimakon Ubangiji (SWT) a kan dukkan wasu lamurran siyasar kasar.

Babangida, ya bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da ya yi da manema labarai a Minna babban birnin jihar Neja, a wani bangare na bikin zagayowar ranar haihuwarsa.

A cikin jawaban nasa, tsohon shugaban kasar, ya bukaci ‘yan Najeriya a kan su ci gaba yin amanna a kan hadin kan kasa, sannan kuma su sanya a ransu cewa komai zai daidaita da sannu a hankali.

Ya ce “Ina rokonku a kan ku rinka hakuri da juna, kuma ku ci gaba da addu’a don neman daukin Ubangiji a game da wasu lamurra da suka shafi al’muran rayuwa da kuma siyasa.”

Tsohon shugaban na Najeriya, ya ce akwai bukatar a ci gaba da wayar da kan jama’a a kan yadda za su zauna lafiya da juna da kuma samun ci gaba mai dorewa.

Ya kuma shawarci ‘yan jarida a kan su goyi bayan yunkurin da ake na hada kan kasa.

Ya ce, idan har ‘yan jarida za suyi watsi da masu yada jita-jita, to ko shakka ba bu za su samu hanyoyin isar da sakonninsu yadda ya dace.

Kuna abin da ya dace wajen kokarin hada kan kasa da ma sauya al’ummar Najeriya, in ji shi. In ji BBC.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp