fidelitybank

Ƙwalara da cutar Sanƙarau sun kashe mutane 32 a Najeriya – WHO

Date:

Hukumar lafiya ta Duniya (WHO), ta ce, kimanin mutum 922 ne aka bayyana cewa, sun kamu da cutar kwalara ko amai da gudawa a Najeriya, yayin da mutum 32 suka mutu sakamon cutar a shakerar 2023 da muke ciki.

A wani rahoton da WHO ta fitar, ta ce, zuwa 5 ga watan Maris 2023 yawan mace-mace sakamakon cutar ya kai kashi 3.5 cikin 100

WHO ɗin ta kuma ce, alƙaluman sun haɗar da waɗanda suka bayyana alamun cutar, da kuma waɗanda aka tabbatar da cewa sun kamu a ɗakunan gwajin cutar da ke asibitocin ƙasar.

Ta kuma ce alƙaluman ka iya sauyawa a kowanne lokaci sakamakon rahotonnin da ake samu a mabambantan wurare a faɗin ƙasar.

Cutar Kwalara ko amai da gudawa, cuta ce da ake kamuwa da ita sakamakon ɗaukar ƙwayar cutar ‘cholerae bacteria’, mutum kan kamu da cutar idan ya ci abinci ko ya sha ruwan da ke ɗauke da ƙwayar cutar.

Cutar dai kan zo da tsanani wanda a wasu lokutan ma take barazana ga rayuwar wanda ya kamu da ita, matuƙar bai samu kulawar gaggawa ba.

A wani labarin na daban kuma wani rahoto da hukumar daƙile yaduwar cutuka ta Najeriya NCDC ta wallafa a shafinta na intanet, ya nuna cewa an tabbatar da samun mutum 157 da ke ɗauke da cutar sankarau tsakanin watan Oktoban bara zuwa watan Maris da muke ciki.

Haka kuma an samu marasa lafiya da ake zargin sun kamu da cutar su kusan 628, ciki har da mutum 52 da suka mutu a jihohin ƙasar 21.

Alamomin cutar sun haɗar da zazzaɓi da ciwon kai da tashin zuciya da amai, da sanƙarewar wuya.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp