Shugabannin kwadago za su gudanar da taro da takwarorinsu na rassan kungiyoyin ma’aikata don tattauna batun karin albashin wucin gadi na N35,000 a tsawon wata shida da gwamnatin tarayya ta yi ranar Lahadi ga ma’aikatan tarayya.
Shugaba babbar kungiyar kwadago ta NLC, Kwamared Joe Ajaero ne ya sanar da haka lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa, bayan wani taro na tsawon sa’a hudu da jami’an gwamnati karkashin jagorancin shugaban ma’aikatan fadar, Mista Femi Gbajabiamila.
Kwamared Ajaero ya ce kungiyoyin kwadago su kadai, ba za su iya dakatar da shiga yajin sai-baba-ta-gani da suka tsara farawa daga gobe Talata ba, sai fa idan sun tuntubi rassan kungiyoyin wakilansu.
Ya ce sun gudanar da taro kuma sun duba kusan dukkan batutuwan da ake dambarwa a kansu da kuma alkawurran da gwamnati ta yi, da hanyoyin da za a bi don tabbatar da ganin an cika su.
Don haka za mu je, mu kia wa ma’aikatan da muke wakilta wadannan alkawurra kafin zartar da wata sabuwar matsaya.