fidelitybank

Ƙungiyoyin ƙwadago na barazana a Rivers

Date:

Ƙungiyoyin ƙwadago na NLC, TUC da JNC reshen jihar Rivers sun yi barazanar ɗaukar mataki muddin gwamnatin Najeriya ba ta janye dokar-ta-ɓaci a jihar Rivers ba.

Shugabannin ƙungiyoyin na jihar sun nuna damuwa kan tasirin dokar-ta-ɓacin a kan tattalin arzikin jihar da kuma nuna rashin dacewar ta a hukumance.

Matakin ya sanya an kasa biyan albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi a jihar, a cewar su.

Ƴan ƙwadagon sun bayyana cewa dakatar da zaɓaɓɓun jami’an gwamnatin jihar da rashin biyan albashin ma’aikatan keta haƙƙin bil’adama ne da ka iya ta’azzara matsalar tsaro da na tattalin arziki a jihar.

Sanarwar da ƙungiyoyin suka sanya wa hannun ta yi kira ga shugaban Najeriya da majalisar dokoki da kuma ɓangaren shari’a da su ɗauki matakan janye dokar nan take tare da mayar da gwamnan jihar da mataimakiyarsa da kuma ƴanmajalisar jihar.

Idan kuma ba a yi hakan ba nan da wani lokaci, a cewarsu, za su ɗauki matakan da ka iya shafar tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp