fidelitybank

Ƙungiyar tuntuɓa ta arewa ta buƙaci a biya diyyar waɗanda aka kashe a Filato

Date:

Ƙungiyar tuntuɓa ta arewa wato Arewa Consultative Forum (ACF) ta bayyana rashin jin daɗinta kan hare-haren da ke faruwa a jihar Filato ta arewacin Najeriya, inda a kwanakin baya aka kashe mutane da dama, ciki har da ƙananan yara da mata.

A wata sanarwa da sakataren watsa labarai na ƙungiyar, Tukur Muhammad-Baba ya fitar, ƙungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta sanya dokar ta-ɓaci a yankunan da ke fama da hare-haren na ƴanbindiga.

“A bayyana yake mutanen jihar na cikin tsananin tashin hankali, wanda kuma ya zo a daidai lokacin da rayuwa ta yi tsada. Dole ne a kawo ƙarshen kashe-kashen nan, sannan dole a tabbatar an dawo da zaman lafiya a jihar,” in ji ƙungiyar, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Ƙungiyar ta kuma yi kira da a ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri, sannan a ƙara ƙarfafa jami’an tsaro wajen bibiya tare da kama masu laifi, “sannan su yi bincike domin a hukunta waɗanda aka samu da laifi.”

Haka kuma ACF ta buƙaci a tabbatar da biyan diyya ga wadanda suka rasa ƴanuwansu, sannan a tallafa wa waɗanda suka jikkata.

A ƙarshe ƙungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jihohi su ƙarfafa malaman addini da masu riƙe da sarautun gargajiya da ƙungiyoyi masu zaman kansu da sauran masu ruwa da tsaki domin taimakawa wajen sulhunta ɓangarori.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp