Ƙungiyar tuntuɓa ta arewa wato Arewa Consultative Forum (ACF) ta bayyana rashin jin daɗinta kan hare-haren da ke faruwa a jihar Filato ta arewacin Najeriya, inda a kwanakin baya aka kashe mutane da dama, ciki har da ƙananan yara da mata.
A wata sanarwa da sakataren watsa labarai na ƙungiyar, Tukur Muhammad-Baba ya fitar, ƙungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta sanya dokar ta-ɓaci a yankunan da ke fama da hare-haren na ƴanbindiga.
“A bayyana yake mutanen jihar na cikin tsananin tashin hankali, wanda kuma ya zo a daidai lokacin da rayuwa ta yi tsada. Dole ne a kawo ƙarshen kashe-kashen nan, sannan dole a tabbatar an dawo da zaman lafiya a jihar,” in ji ƙungiyar, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.
Ƙungiyar ta kuma yi kira da a ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri, sannan a ƙara ƙarfafa jami’an tsaro wajen bibiya tare da kama masu laifi, “sannan su yi bincike domin a hukunta waɗanda aka samu da laifi.”
Haka kuma ACF ta buƙaci a tabbatar da biyan diyya ga wadanda suka rasa ƴanuwansu, sannan a tallafa wa waɗanda suka jikkata.
A ƙarshe ƙungiyar ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jihohi su ƙarfafa malaman addini da masu riƙe da sarautun gargajiya da ƙungiyoyi masu zaman kansu da sauran masu ruwa da tsaki domin taimakawa wajen sulhunta ɓangarori.