fidelitybank

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta baiwa Falasɗinu tallafin Yuro biliyan 1.6

Date:

Kungiyar Tarayyar Turai ta ce za ta bunkasa tallafin kudi ga Hukumar Falasdinu da wani kunshin shekaru uku na kusan Euro biliyan 1.6 (dala biliyan 1.8).

Kwamishinan Tarayyar Turai mai kula da tekun Mediterrenean Dubravka Suica, ya ce tallafin kudi zai tafi kafada da kafada da sauye-sauyen hukumar Falasdinu, wadda masu sukar almundahana da rashin gudanar da mulki ke zargi.

Suica ta ce “Muna son su gyara kansu domin ba tare da gyara ba, ba za su kasance masu karfi da gaskiya ba domin su zama masu shiga tsakani, ba don mu kadai ba, har ma da Isra’ila,” in ji Suica.

Wannan dai na zuwa ne gabanin wata babbar tattaunawa ta siyasa ta farko tsakanin ministocin harkokin wajen Tarayyar Turai da manyan jami’an Falasdinawa ciki har da firaminista Mohammad Mustafa a Luxembourg ranar Litinin.

EU ita ce babbar mai ba da taimako ga Falasdinawan kuma jami’an EU na fatan hukumar Palasdinawa mai kula da gabar yammacin kogin Jordan, ita ma wata rana za ta iya daukar nauyin Gaza bayan an kawo karshen yakin da ake yi tsakanin Isra’ila da mayakan Hamas.

Sai dai gwamnatin firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya zuwa yanzu, ta yi watsi da ra’ayin mika Gaza ga hukumar Falasdinu, tare da yin watsi da babban burin kungiyar EU na samar da kasashe biyu, wanda zai hada da kafa kasar Falasdinu.

A cewar Suica, Euro miliyan 620 za ta je ne ga tallafin kudi da yin gyare-gyare ga hukumar Falasdinu, da Euro miliyan 576 don jurewa da farfado da yankin yammacin kogin Jordan da Gaza da kuma Euro miliyan 400 za a samu lamuni daga bankin zuba jari na Turai, bisa amincewar hukumar gudanarwarta.

Ta kara da cewa matsakaita tallafin da EU ke baiwa hukumar Falasdinu ya kai kimanin Euro miliyan 400 cikin shekaru 12 da suka gabata.

Suica ta ce “Yanzu muna saka hannun jari cikin sahihiyar hanya a Hukumar Falasdinawa.”

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp