fidelitybank

Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta zama mamba a ƙungiyar G-20

Date:

Kungiyar Tarayyar Afirka, AU, ta zama mamba ta dindindin a G-20 da ake kira Group of 20.

Firayim Ministan Indiya, Narendra Modi ne ya sanar da hakan a yau Asabar yayin da yake bude taron shugabannin a New Delhi, babban birnin Indiya na kasashe mafiya arziki a duniya.

A yayin jawabin bude taron, firaministan Indiya ya gayyaci shugaban kungiyar Tarayyar Afirka, Azali Assoumani, da ya hau kujerarsa a matsayin mamba na dindindin a kungiyar.

A cikin jawabinsa na bude taron, Modi ya ce “a yau, a matsayinsa na shugaban G-20, Indiya ta yi kira ga duniya da ta taru don sauya gibin amana a duniya zuwa aminci da dogaro.”

“Wannan ne lokacin da dukan mu za mu matsa tare. Ya zama rarrabuwar kawuna tsakanin Arewa da Kudu, tazarar da ke tsakanin Gabas da Yamma, sarrafa abinci da man fetur, ta’addanci, tsaro ta yanar gizo, lafiya, makamashi ko tsaro na ruwa, dole ne mu nemo mafita ga wannan al’umma masu zuwa.”

Kafin taron, G-20 wani taro ne da ya kunshi kasashe 19 da suka hada da Tarayyar Turai.

Rukunin na 20 yana aiki don magance manyan batutuwan da suka shafi tattalin arzikin duniya, kamar kwanciyar hankali na kudi na kasa da kasa, rage sauyin yanayi da ci gaba mai dorewa.

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya bar kasar zuwa Indiya ranar Talata gabanin taron.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp