Kungiyar masana fasahar kere-kere ta kasa (NAAT) a ranar Lahadin da ta gabata ta umurci mambobinta da su fara yajin aikin gargadi na mako biyu a ranar Litinin.
Shugaban NAAT, Ibeji Nwokoma, a wata sanarwa, ya yi zargin gazawar gwamnatin tarayya wajen aiwatar da yarjejeniyar 2009.
Ya ce, wa’adin kwanaki 14 da aka baiwa gwamnati ya wuce.
Ya kuma ce, wani taron majalisar zartaswar kungiyar ta kasa ya yanke shawarar rufe dukkan dakunan gwaje-gwaje, wuraren bita, dakunan karatu da kuma gonaki na tsawon lokacin yajin aikin gargadi. In ji Daily Trust.