Kungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta kasa, ta ce , mambobinta za su shiga yajin aikin da ake shirin yi a fadin kasar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa na yajin aiki na dindindin a fadin kasar mai dauke da sa hannun sakataren ta T. A. Shettima da shugaban kasa Nnachi Michael Ekuma da mataimakin shugaban kasa Shehu Abubakar da dai sauransu.
“Za ku iya tunawa gwamnatin tarayya ta sanar da cire tallafin man fetur a lokacin rantsar da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, a watan Mayun 2023,” in ji wasikar.
Matakin da shugaban kasar ya dauka ya gamu da cikas ga ma’aikatan Najeriya da marasa galihu.
“Shugabannin NLC sun sanya bukatu da yawa a matsayin hanyar da za ta rage wa ma’aikatan Najeriya wahala ba tare da samun nasara ba.
“Shugabannin kungiyar kwadagon Najeriya sun kaddamar da ayyuka da dama, tun daga zanga-zangar kin jinin gwamnati, yajin aikin gargadi na kwanaki 3, har ma da wa’adin kwanaki 3, amma har yanzu gwamnatin tarayya ta yi kunnen uwar shegu da gargadin kungiyar NLC.
“Saboda haka, shugabannin kungiyar Kwadago ta Najeriya sun yi taro a ranar Talata 26 ga Satumba, 2023 inda suka yanke shawarar fara yajin aikin sai baba-ta-gani.
“Bisa abubuwan da ke sama, an umarce ni da in gabatar da shawarar da kungiyar kwadago ta kasa NLC ta yanke na fara ayyukan masana’antu na kasa baki daya daga ranar Talata 3 ga Oktoba.”