fidelitybank

Ƙungiyar Gwamnoni ta aike da wasika ga gwamnatin tarayya a kan kudin Paris Club

Date:

Ƙungiyar Gwamnonin jihohin ƙasar nan, sun sake yin watsi da yunkurin fara cire kudaden Paris Club da suka kai dala miliyan 418, daga asusun tarayya, domin biyan wasu ‘yan kwangila.

Kungiyar gwamnonin ta aika wa gwamnatin tarayya wata wasika, inda ta ce taɓa kudaden waɗanda suke ƙalubalantar batun a gaban kotu, karan tsaye ne ga kundin tsarin mulkin kasa.

A wata wasika da ta aikewa gwamnatin tarayya, ƙungiyar gwamnonin ta bayar da hujjar cewa, duk wani yunƙurin daukar matakan fara zaftare kudaden, sun saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasa, tun da ana shari’a a kan maganar.

Ta ce, kuma tuni ma kotu Ƙoli ta fadi matsayinta a kan batun.

Shugaban ƙungiyar, kuma gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi ne ya sanya hannu kan wasiƙar.

Sannan ƙungiyar gwamnonin na ganin lamunin da aka bayar tun da farko, wanda gwamnatin tarayya ta shiga tsakani, kuma ake maganar sake fara cire shi, an bayar da shi ne bisa kuskure ta hannun wasu ƴan kwangila.

Sai dai har yanzu gwamnati ba ta ce komai ba game da wasiƙar da ƙungiyar gwamnonin suka aike mata.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp