Shugabannin ƙungiyar ƙasashen Afirka ta Yamma Ecowas za su gana yau Lahadi a Abuja, domin tattauna batutuwan da suka shafi haɗin kai da tsaro da kuma tattalin arzikin yankin.
Ana sa ran batun ficewar ƙasashen yankin Sahel daga ƙungiyar ne zai zama babban manifar taron na yau.
Ƙa’idar da Ecowas ta gindaya ta sanarwar shekara guda kafin ficewar ƙasa daga ƙungiyar wanda ƙasashen Mali da Burkina Faso da Nijar suka yi, zai cika a watan Janairu mai zuwa.
A makon da ya gabata ne, shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya shaida wa shugaban Jamus da ya ziyarci ƙasar, Frank-Walter Steinmeier, cewa muradun walwalar ‘yan ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar ne babban abin da ke ran shugabannin Ecowas.
Inda ya alƙawarta yi amfani da diplomasiyya da hikima wajen maido da ƙasashen cikin ƙungiyar.
Shugaba Tinubu – wanda shi ne shugaban Ecowas – ya sha amfani da hanyoyin diflomasiyya don ganin ya janyo hankalin ƙasashen na yankin Sahel domin su koma cikin ƙungiyar.