fidelitybank

Ƙungiyar ƙwadago ta yi watsi da tuƙuicin Naira dubu 10 da za baiwa ma’aikatan Jigawa

Date:

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa reshen jihar Jigawa ta yi watsi da tukwicin 10,000 da gwamnatin jihar za ta bai wa ma’aikatanta a matsayin kuɗin rage raɗaɗin cire tallafin man fetur.

Wannan yana kunshe a cikin wata sanarwar da aka saki bayan kammala taron kungiyar da aka yi ranar Talata a Dutse.

Sanarwar wadda shugabannin kananan hukumomi da kuma sakatarorin ƙungiyar ƴan kwadago ta NLC da TUC reshen jihar suka saka hannu ta fasalta yadda gwamnatin ta yi azarɓaɓin yanke hukunci kan bada tukwicin tun da ba su cimma yarjejeniya ba.

A farkon makon nan ne dai gwamnan jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ya amince da biyan ma’aikatan jihar kudi 10,000 a duk wata a tsawon watanni uku, kafin gwamnatin tarayya ta fito da tsarin sabon albashi.

A makon da ya gabata ne dai gwamnatin tarayyar karkashin mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya kaddamar da kwamitin domin yin duba ga albashin da ake biya mafi kankanta a Najeriya.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp