Kungiyar ‘yan kasuwan Arewa maso Gabas, ta siyawa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar fom din tsayawa takarar shugaban kasa a shekarar 2023 domin ya tsaya takara a jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP).
Tun a watan Disambar 2021 ƙungiyar ta yi alkawarin sayan fom ga tsohon mataimakin shugaban kasa a matsayin nuna goyon bayansu ga takararsa ta shugaban kasa.
Shugaban kungiyar ‘yan kasuwa ta Arewa maso Gabas, Abubakar Dalhatu Funakaye, wanda ya gabatar da fom din a madadin kungiyar, ya baiwa tsohon mataimakin shugaban kasar tabbacin marawa baya a yunkurinsa na shugabancin Najeriya.
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2019, wanda ya yaba wa taron, ya bukaci su da sauran ‘yan Najeriya da su hada kai, wajen magance dimbin kalubalen da Najeriya ke fuskanta.