Sanarwar ƙarshe ta taron ƙasashen Larabawa da na Musulmi 57 da ya gudana a Saudiyya ya nuna cewa ɗaukacin ƙasashen sun buƙaci a tsayar da rikicin Gaza nan take.
Mai masaukin baƙi Saudiyya ta zargi ƙasashen duniya da nuna bambanci tsakanin ƙasashe.
Ministan harkokin waje na Saudiyya ya ce kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya gaza wajen sauke nauyin da ke kansa saboda ya gaza hukunta Isra’ila kan abubuwan da ta aikata.