fidelitybank

Ƙasashen ECOWAS za su tattauna kan harajin ƙasashen yankin Sahel

Date:

Ƙungiyar ECOWAS za ta gudanar da taron na musamman domin tattaunawa kan harajin kayayyaki da ƙungiyar ƙasashen AES suka lafta wa ƙasashenta.

Ƙasashen ECOWAS za su zauna ne a watan da ake ciki na Afrilu, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito daga jami’in watsa labarai na ƙungiyar ƙasashen Joel Ahofodji.

Ya ce, “za a yi taron ne a ranar 22 ga Afrilu kan harajin kashi 0.5 da ƙasashen AES suka lafta wa kayayyakin da ke shiga ƙasashensu da su daga ƙasashen ECOWAS.”

Da aka tambaye shi ko akwai yiwuwar ƙungiyar ECOWAS ɗin za ta mayar da martani wajen ɗora wa ƙasashen na AES haraji, sai ya ce, “a lokacin taron za a tattauna komai da komai.”

Ƙasashen AES wato Mali da Nijar da Burkina Faso da suke ƙarƙashin mulkin soji ne suka sanar da ɗora wa ƙasashen ƙungiyar ECOWAS da suka fice harajin kashi 0.5 kan kayayyakin da ake shiga da su, “domin samun kuɗaɗen shiga.”

Harajin zai fara aiki ne daga ranar 28 ga watan Maris, amma banda kayayyakin agaji.

Wannan ya saɓa da yadda aka saba na cinikayya da shiga da fitar da kayayyaki ba tare da shinge ba a tsakanin ƙasashen ECOWAS.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp