fidelitybank

Ƙasashen da suka kai matakin zagaye na gaba a kofin duniya

Date:

A ranar Juma’a za a kammala buga wasannin zagayen farko na gasar cin kofin duniya da ake fafatawa a Qatar.

Kawo yanzu wasu kasashen sun tsallake zuwa zagaye na biyu wasu kuma an fitar da su. In ji BBC.

A yayin da akwai wasu karin kasashen da suma za su iya kaiwa mataki na gaba.

Rukunin A

A wannan rukunin kasashen Netherlands da Senegal su ne za su buga wasanni a zagaye na biyu.

A yayin da mai masaukin baki Qatar da Ecuador kuma aka fitar da su.

Rukunin B

Ingila da Amurka su ne suka haye zuwa mataki na gaba a yayin da Iran da Wales kuma aka fitar da su.

Rukunin C

Argentina da Poland su ne kasashen da suka yi nasarar tsallakewa zuwa mataki na gaba a gasar.

A yayin da Saudi Arabiya da kuma Mexico suka fita daga cikin gasar.

Rukunin D

Faransa da Australiya su ne kasashe biyu da suka fito daga wannan rukunin duk da cewa Tunisia ta doke Faransar a wasansu na karshe.

Denmark da Tunisia su ne suka gamu da rashin sa’a a wannan rukunin.

Rukunin E

Spaniya da Costa Rica da Japan da kuma Jamus su ne a wannan rukunin. Amma kawo yanzu babu wacce ta tsallake zuwa zagaye na biyu. Sai a wasanninsu na yau za a sani.

Spaniya za ta kara da Japan sai kuma Jamus ta hadu da Costa Rica.

Rukunin F

Croatia da Belgium da Canada da Morocco su ne a wannan rukunin.

Canada ta riga ta san makomarta saboda an doke ta a wasanni biyu na farko saboda haka ba za ta kai zagaye na gaba ba.

Rukunin G

Brazil ta tsallake zuwa zagaye na biyu.

Sai dai a ranar Juma’a za a san tsakanin Switzerland da Kamaru da Serbiya kasar da za ta kai mataki na gaba.

Rukunin H

Portugal ta kai matakin zagaye na biyu a gasar bayan ta samu nasara a wasanni biyu a jere.

Ghana da Koriya ta Kudu da Uruguay su ne sauran kasashen da ke a rukunin kuma a cikinsu kasa daya ce za ta iya kai wa mataki na gaba.

Kasashe 16 ne za su kai mataki na biyu a gasar cin kofin duniya.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...
X whatsapp