A yau ne da karfe 6 na yamma za a fara zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a babban taron jam’iyyar na kasa a Abuja.
Kamar yadda jadawalin ya nuna, ana sa ran wakilan da suka cancanta daga jihohin kasar nan 36 da kuma babban birnin tarayya Abuja, za su isa wurin da misalin karfe 10 na safe zuwa karfe 1 na rana.
Wurin da za a gudanar da babban taron jam’iyyar APC na kasa a dandalin Eagle Square dake Abuja.
Jadawalin taron da jam’iyyar ta fitar, ya nuna cewa shugaban jam’iyyar na kasa Abdullahi Adamu zai gabatar da jawabin maraba da misalin karfe 3:40 na rana.
A halin da ake ciki, za a bar masu neman shugabancin kasar su gabatar da jawabansu tsakanin karfe 4:45 na yamma zuwa 5:45 na yamma.
Buhari zai gabatar da jawabinsa da karfe 5:45 na yamma. Wakilan za su fara kada kuri’a daga karfe 6 na yamma zuwa karfe 9 na yamma, yayin da za a bayyana sakamakon da karfe 10 na dare.