fidelitybank

Ƙarancin wutar lantarki ya sanya minista taron gaggawa a Najeriya

Date:

Ministan harkokin lantarkin, Inijiniya Abubakar D. Aliyu, ya kira taron gaggawa na masu ruwa da tsaki, domin samar da mafita dangane da matsalar wutar lantarkin Najeriya.

Taron ya kunshi kamfanonin samar da wutar lantarki da kuma hukumomi na gwamnati da masu zaman kansu da suke da ruwa da tsaki a harkar samar da wutar lantarki da iskar gas.

Taron, wanda aka gudanar a Abuja, Injiya Abubakar D. Aliyu ya ce, gwamnati ba za ta amince ba da yadda lamarin wutar lantarki ya samu koma baya, ya na mai cewa, dole a samo mafita ga dukkan matsalolin da suke kawo koma baya ga yawan wutar lantarki da ‘yan Najeriya suke samu a kullum.

Ministan ya kuma gargadi hukumomi da kamfanoni na harkar wutar lantarki su guji nunawa juna yatsa, su mayar da hankali wajen tallafawa juna wajen tabbatar da cewa ‘yan Najeriya suna samun isasshiyar wutar lantarki.

Taron ya mayar da hankali ne ga duba dukkan matsalolin da suke kawo koma baya ga harkar wutar lantarki a Nijeriya.

Injiniya Abubakar D. Aliyu ya ce, gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari, za ta ci gaba da kokarin daukar matakai, domin ganin cewa an samu karuwar wutar lantarkin da ake samarwa a Najeriya. In ji BBC.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp