Gwamnatin tarayya ta ce, karancin ruwan da ake samu a madatsun ruwa ne ke haddasa rashin wutar lantarki a kasar.
Ministan wutar lantarki, Abubakar Aliyu, ya bayyana cewa, noman rani ya haifar da raguwar karfin ruwa na madatsun ruwa.
Aliyu, wanda ya bayyana hakan a wajen taron karawa juna sani da kungiyar ‘yan jarida ta shugaban kasa ta shirya a ranar Alhamis a Abuja, ya ce, “Ina so in tattauna batun karin lodin da aka samu. Wataƙila kun lura a Abuja da sauran yankunan ƙasar.
Tare da raguwar karfin ruwa a lokacin rani, ana bukatar karin kaya daga kamfanonin iskar gas din mu,” inji shi.
Ministan ya kuma bayyana cewa, aikin kula da wasu cibiyoyin samar da wutar lantarki a fadin kasar nan ya taimaka wajen rage wutar lantarki.