Kamfanin mai na ƙasa, NNPCL, ya ce, tsaikon da aka samu wajen fito da man fetur daga jiragen dakon man da ke bakin teku ne ya haddasa ƙarancin man a biranen Abuja da Legas.
Cikin wata sanarwa da kamfanin ya wallafa a shafinsa na X ya ce tsaikon fito da man ya janyo cikas wajen rarraba shi zuwa wasu sassan biranen Abuja da Legas.
Kamfanin ya kuma ce yana ƙoƙarin tuntuɓar masu ruwa da tsaki don ganin ya shawo kan matsalar, ta yadda za a riƙa fito da man a kan lokaci, domin ci gaba da rarraba man zuwa yankunan.
Najeriyar dai kan shigo da man da take amfani da shi daga ƙasashen ƙetare ta jiragen ruwa.
A ‘yan kwanakin biyun nan dai an riƙa ganin layukan ababen hawa a wasu gidajen man birnin Abuja.