fidelitybank

Ɗan Pantami ya shaƙi iskar ƴanci sa’o’i 24 bayan sace shi

Date:

 

 

 

Ali Isa Ali, ɗan Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki ta Fasahar Zamani, Isa Ali Pantami, ya shaƙi iskar ƴanci, sa’o’i 24 bayan da a ka ce an sace shi.

Jaridar Nation ta rawaito cewa an tsinci Ali, ɗan shekara 14 a wani shingen binciken jami’an tsaro a Ƙaramar Hukumar Dambam, Jihar Bauchi.

An rawaito cewa an yi garkuwa da Ali ne a kan hanyar shi ta dawowa gida bayan an tashe su da ga makarantar islamiyya, inda masu garkuwar da shi su ka yi awon-gaba da shi a kan babur.

Jaridar ta ce babu wani cikakken bayani kan yadda yaron ya kuɓuta, inda ya ke zaune wajen mahaifiyarsa a Bauchi bayan da a ke zargin sun rabu da Pantami.

Nation ta ƙara da cewa mahaifiyar taron ma ta tabbatar da kubutar ta sa, inda ta ce tuni ya na gida tare da ita.

Haka shima Babban Limamin Masallacin Juma’a na Isa Ali, Imam Hussain ya tabbatar da cewa Ali ya kuɓuta kuma ya na wajen mahaifiyarsa.

Jaridar ta ƙarar da cewa da a ka tuntuɓi Kwamishinan Ƴan Sanda na Jihar Bauchi, Ahmed Mohammed Wakil, ya ce bashi da masaniyar sace yaron sabo da ba a kai rahoton ga ƴan sanda ba.

Ya ce ya tuntuɓi caji-ofisoshi cikin garin Bauchi amma duk sun ce basu da masaniya kan lamarin.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp