fidelitybank

Ɓarawo ya rasu ya na ƙoƙarin yin sata a ƙarƙashin mota

Date:

 

 

An tsinci gawar wani mutum da a ke zargin ɓarawo ne a ƙarƙashin wata mota a Ago Egun, bodar Idiroko da ke Jihar Ogun.

Jaridar Tribune ta rawaito cewa a na zargin ɓarawon ya yi yunƙurin kwance wasu muhimman abubuwa a jikin motar, amma sai jak ɗin ɗaga mota da ya yi amfani da shi wajen ɗaga motar ya goce bayan ya riga ya shiga ƙarƙashin ta, inda motar ta faɗo masa.

Soji Gonzalo, Kwamandan rundunar bijilante ta jihar, ya baiyana cewa su na cikin sintiri ne sai su ka ga gawar mutum a ƙarƙashin wata tsohuwar mota a wani garejin gyaran mota.

Ya ƙara da cewa sun gano gawar mutumin ne da misalin ƙarfe 6 na yamma a Ago Egun ranar Alhamis.

Gonazlo ya baiyana cewa binciken su na farko ya nuna cewa motar ta daɗe a garejin wanda sama da shekara biyu ba amfani da shi kuma duk yi kurin samun wanda ya ke da filin garejin ya ci tura.

“A yanzu dai mun ɗauke gawar da kuma jak da mu ka samu mai launin ja da kuma almakashi da sauran sifanu za mu kai wa ofishin ƴan sanda na Idiroko domin faɗaɗa bincike,” in ji Gonzalo.

 

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...
X whatsapp