Jami’an ƴansandan jihar Kebbi, sun ƙi karɓar cin hancin naira miliyan ɗaya daga wasu waɗanda ake zargi suna da alaƙa da ƴan Lakurawa.
A wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar Kebbi, Nafiu Abubakar, ya fitar, ya ce mutum uku: Umaru Garba daga ƙauyen Ɗangandu da Abubakar Mamman daga Maimaichi da Usman Muhammadu daga ƙauyen Bakaramba ne aka kama da laifin.
Kakakin ya ce sun ba babban jami’in binciken wani ta’addanci da ake zargin ƴan Lakurawa da aikatawa a arewacin jihar Kebbi, inda suka kai kuɗin domin a rufe binciken.
Ya ce ana cigaba da gudanar da binciken, sannan da zarar an kammala za a tura su kotu.