fidelitybank

Ƴanbindiga sun sace wanda ya lashe gasar karatun Al-Qur’ani ta Najeriya

Date:

Ƴanbindiga sun sace mutumin da ya zama zakaran gasar karatun al’qur’ani ta bana tare da danginsa a kan hanyar Faskari zuwa ƴankara a jihar Katsina.

Shugaban ƙaramar hukumar Faskari, Hon Musa Ado Faskari ya shaida wa BBC faruwar lamarin, inda ya ce ƴanbindigar sun sace Abdulsalam Rabi’u Faskari tare da mahaifinsa da ƴan’uwansa a lokacin da suke kan hanyar komawa gida bayan sun halarci fadar gwamnatin Katsina inda gwamna ya karrama gwarzon.

Hon. Musa Faskari ya ce gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Umaru Radda ne ya gayyaci , Abdulsalam Rabi’u Faskari tare da iyalansa ciki har da mahaifinsa a ƴan’uwansa, domin karrama shi bisa nasarar da ya samu ta zama gwarzon gasar karatun al-qur’ani da aka kammala a jihar Kebbi.

”A kan hanyarsu ta komawa gida ne, sun baro Funtua a kan hanyar Faskari zuwa ƴankara , ƴanbindiga suka tare su tare da yin garkuwa su duka, sai mutum guda da ya samu nasarar kuɓuta”, in ji shugaban ƙaramar hukumar.

Ya ce lamarin ya rutsa da aƙalla mutum bakwai – waɗanda duka dangin juna ne, sai abokin gwarzon gasar guda, wanda shi ma ya halarci taron karramawar.

Ya ƙara da cewa hukumomi na ci gaba da neman mutanen domin kuɓutar da su cikin ƙoshin lafiya.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp