fidelitybank

Ƴanbindiga sun sace fasinjoji sama da asirin a jihar Neja

Date:

An sace fasinjoji sama da ashirin a wasu motoci biyar a kan hanyar Mariga zuwa Kontagora da ke jihar Naija.

Shugaban majalisar dokokin jihar wanda kuma shi ne wakilin mazaɓar Mariga inda lamarin ya faru, Abdulmalik Sarkin-Daji ya tabbatar da labarin ga manema labarai, kamar yadda jaridar Dailt Trust ta ruwaito.

Ya ce ɓarayin sun datse hanyar ne ta Mariga zuwa Kontagora a shekaran jiya Alhamis a daidai titin Babbar-Lamba da Beri inda suka yi awon-gaba da fasinjojin.

Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake mayar da martani kan yadda sojojin Najerya suka musanta labarin da ke cewa ɓarayin daji sun kama sansanin horonsu a yankin ƙaramar hukumar Kontagora, yankin da ya kai har Mariga.

Abdlmalik ya ce, iyalan waɗanda aka sace a baya suna kai wa ɓarayin dajin kuɗin fansa sau da dama a cikin dajin, wanda ya ce ɓangare ne na sansanin atisayen sojin.

Ya ce wasu daga cikin waɗanda ɓarayin ke garkuwa da su sun gaya wa ‘yan uwansu cewqa an tsare su ne dajin da ba shi da nisa da barikin soji na Kontagora.

Shugaban ya ce su ma waɗanda aka sace ranar Alahamis an kai su dajin ne, inda ya yi kira ga hukumomin sojin na Najeriya da su nemi bayanai na gaskiya su je su kawar da waɗannan ɓarayin daji.

Jariadr ta ce, kakakin rundunar ‘yansandan jihar ta Naija Wasiu Abiodun ya ce zai samo cikakken bayanin satar mutanen kafin ya yi magana amma kuma ba a ji shi ba.

nigerianewspapers.com.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp