fidelitybank

Ƴanbindiga sun kashe Jami’an sa kai 15 a Katsina

Date:

Rundunar ƴansandan jihar Katsina ta tabbatar da kai wani hari kan wasu jami’an ƙungiyar tsaro ta Community Watch Corps a jihar, wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 25.

Lamarin ya faru ne ranar Laraba lokacin da jami’an tsaron na Community Watch Corps, suka yi zango a garin Ɓaure na jihar ta Katsina, bayan ziyarar ta’aziyar ɗaya daga cikin abokin aikinsu da ya mutu sakamakon harin ’yanbindigar.

Ɗaya daga cikin waɗanda suka shida lamarin ya shaida wa BBC cewa kwantan ɓunar-da ‘yanbindigar suka yi wa jami’an ya janyo mutuwar fiye jami’an na Community Watch Corps 10.

‘’Bayan sun tsaya ne, sai kwatsam ‘yanbindigar suka buɗe musu wuta, kuma sun kashe aƙalla mutum 15’’, in ji shi.

Ya kuma ce bayan kashe mutanen ‘yanbidigar sun hana a ɗauki gawarwakinsu har sai ranar Alhamis da safe.

Bayan kashe jami’an tsaron na ‘Community Watch Corps’, mutanen gari sun fantsama kasancewar ranar kasuwar gari ne, lamarin da ya sa aka kashe wasu daga cikinsu, inda har yanzu ba a ga wasu mutanen ba kamar yadda wasu mazauna yankin suka bayyana wa BBC.

‘’Sun kashe mutanen ƙauyukan yankin masu yawa, aƙalla mutanen da suka kashe sun kai mutum 25’’, a cewar wani da ya shaida lamarin.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Katsina,Abubakar Sadiq Aliyu ya tabbatar wa BBC faruwar lamarin, sai dai ya ce suka ci gaba da tattara bayanai.

Yankunan ƙananan hukmomin Safana da Batsari na daga cikin yankunan jihar Katsina masu mafa da matsalar tsaro.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...
X whatsapp