fidelitybank

Ƴan Sanda sun tsiratar da mutane tara daga hannun ƴan bindiga a Zamfara

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ceto wasu mutane tara da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a kauyen Kucheri da ke karamar hukumar Tsafe a jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Mohammed Shehu, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya bayyana cewa jami’an ‘yan sanda masu dabara a ranar Laraba sun ceto wadanda lamarin ya rutsa da su.

Karanta Wannan: Ƴan Sanda sun kashe ƴan ta’adda biyu tare da ƙwato Shanu a Katsina

Ya yi bayanin cewa, “A ranar 13 ga Afrilu, 2023, rundunar ‘yan sandan dabara ta yi nasarar kubutar da mutane tara – wadanda suka hada da mata bakwai da maza biyu da aka sace a ranar 11 ga Afrilu, 2023 a kauyen Kucheri da ke karamar hukumar Tsafe ta jihar.”

A cewarsa, ceto mutanen ya biyo bayan sahihan bayanai da aka samu daga wani mutumin kirki da ‘yan sanda ke amfani da su, inda suka yi nasarar ceto wadanda lamarin ya rutsa da su.

Ya kara da cewa jami’an ‘yan sanda ne suka yi wa wadanda lamarin ya shafa bayani sannan suka sake haduwa da iyalansu da kuma ‘yan uwansu.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Kolo Yusuf, ya tabbatar wa jama’a da ci gaba da kai farmaki kan ayyukan ‘yan fashi da sauran miyagun laifuka da ‘yan sanda ke yi a jihar.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp