fidelitybank

Ƴan Nijar na zanga-zanga nuna goyon bayan mulkin Soja

Date:

Dubban mutane ne suka gudanar da maci ranar Alhamis a Niamey, babban birnin Nijar don nuna goyon baya ga juyin mulkin da ya kifar da zaɓaɓɓiyar gwamnatin dimokraɗiyya.

Ana zanga-zangar ne yayin da damuwar da ake ita game da tsaro ke ƙaruwa a tsakanin ƙasashen Yamma.

Masu zanga-zanga a tsakiyar birnin Niamey, wasunsu na kaɗa manyan tutocin Rasha, suna rera taken ƙin jinin Faransa a lokacin gangamin, wanda aka kira don bikin samun ‘yancin kan ƙasar daga tsohuwar uwargijiyarta Faransa a 1960.

Gamayyar ƙungiyoyin fararen hula na Nijar sun yi kira ga al’ummar ƙasar su yi watsi da takunkuman karya tattalin arziƙi da Ecowas ta sanya wa Nijar.

Ƙungiyar Ecowas dai ta ce za ta yi amfani da ƙarfin soji matuƙar masu juyin mulkin ba su mayar da Bazoum kan karagar mulki ba.

Duk da wannan nuna goyon baya da fararen hula ke yi wa sojojin, akwai ‘yan Nijar masu yawa da ke adawa da juyin mulkin.

Wasu na zargin cewa sosjojin ne suka kitsa zanga-zangar domin gudun kawar da su daga kan mulki.

To amma yanzu a ƙoƙarinsu na kafa hujja kan juyin mulkin, sojojin na yunƙurin harzuƙa batun ƙin jinin Faransa.

Abin da kuma ya faru kenan a Mali da Burkina Faso, inda jagororin mulkin sojin ke ƙara ƙulla ƙawance da Rasha.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya ruwaito cewa ɗaruruwan matasan riƙe da tutocin ƙasar Rasha sun taru a dandalin samun ‘yanci da ke tsakiyar birnin Yamai.

Issiaka Hamadou ɗaya daga cikin masu zanga-zangar ya ce ”magana ce a kan matsalar tsaro, muna buƙatar taimakon sojoji, kuma muna maraba da shi daga ko’ina ne ba lallai sai Rasha kaɗai ba, ko China ko Turkiyya ne, matuƙar za su taimaka mana”.

“Ba ma son Faransa, waɗanda ke sace mana ma’adanai, tun cikin 1960 suke nan kuma babu abin da ya sauya”, in ji shi.

Faransa na da dakarun soji kimanin 1,500 a Nijar a yaƙin da suke yi da masu iƙirarin jihadi na yankin Sahel.

“Na kasa samun aiki bayan kammala karatu a ƙasar nan, saboda gwamnatin Bazoum da ke samun goyon bayan Faransa,” in ji wani matashi da ya bayyana sunansa da Oumar.

Masu goyon bayan gwamnatin sojin ƙasar na cewa Faransa ta kasa magance musu matsalar masu iƙirarin jihadi, yayin da suke ganin Rasha ce ta fi cancanta da ƙulla ƙawance. A cewar BBC.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...
X whatsapp