Tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Bode George, ya bayyana cewa ‘yan Najeriya na jiran su nunawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kofar ficewa daga zaben shugaban kasa na 2027 mai zuwa cikin matsin tattalin arziki.
George ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a wata sanarwa da ya fitar domin bikin cikarsa shekaru 79 a Legas.
A cewarsa, domin jam’iyyar PDP ta kawar da jam’iyyar All Progressives Congress mai mulki daga kan karagar mulki, dole ne ‘yan kungiyar su hada kai su kawar da kai daga son zuciya.
Ya yi nuni da cewa rikicin da ke faruwa a jam’iyyar adawa ya samo asali ne na son rai da wasu ‘ya’yan jam’iyyar ke kai ta ga halaka.
“Idan muna so mu ci zaben shugaban kasa a 2027, bai kamata mu bari a raba kanmu ba, kuma masu ra’ayin raba kan juna ya kamata a gaya musu da harshe mai haske cewa ‘Ya isa’.
“Tare da irin wahalhalun da ake fama da shi a kasa da kuma tabarbarewar tattalin arziki, ‘yan Najeriya na jiran mu a 2027 don korar APC daga Aso Rock,” in ji shi.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da jam’iyyar PDP ke fafutukar ganin ta ci gaba da wanzuwa bayan da aka dade ana fama da rikicin shugabanci.
Jam’iyyar na shirin gudanar da taron kwamitin zartarwa na kasa karo na 99 wanda aka shirya gudanarwa a ranar 28 ga Nuwamba, 2024.