fidelitybank

Ƴan kama ɓarayin waya a taron APC

Date:

A ranar Talatar nan ne jami’an tsaro suka kama wasu mutane uku da ake zargin sun sace wayar hannu a kofar shiga harabar wajen taron jam’iyyar APC na kasa.

Wadanda ake zargin sanye da tufafi sun yi amfani da hayaniyar da aka yi a kofar dandalin Eagle Square, inda suka dauki wayar daga aljihun dan jarida.

Dan jaridar da aka sakaya sunansa, ya an karar ne bayan ya gano wayarsa ta bace, lamarin da ya ja hankalin jami’an tsaro, inda suka garzaya wurin da lamarin ya faru.

Sai dai ba a iya gano wayar da ta bace ba ko da bayan bincike da aka yi kan mutanen ukun, saboda sun jefa wayar a karkashin wata motar jami’an tsaro da ke kusa da wurin.

Sai dai wani jami’in ya ceto lamarin ya hango wayar a karkashin motar, lamarin da ya sa aka kama wadanda ake zargin.

Wani dan sanda da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce, za a kai wadanda ake zargin zuwa wani ofishin da ke kusa domin gudanar da bincike tare da gurfanar da su gaban kuliya.

A watan Maris ne jami’an tsaro suka kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi ne a babban taron jam’iyyar APC na kasa a Abuja.

Rundunar ‘yan sandan ta kuma kama wasu ‘yan bindiga guda goma a babban taron jam’iyyar PDP a babban filin wasa na kasa a ranar 28 ga watan Mayu.

(NAN)

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp